Ranar Asabar din nan Mai dakin Shugaban Kasa Hajiya Aisha Muhammadu Buhari ta jagoranci kaddamar da yakin menan zaben shekara ta 2019 wanda kwamitin tsare tsaren yakin neman zabe bangaren mata ya gudana a Kano.
Da ta ke gabatar da Jawabinta awuri taron Hajiya Aisha Buhari ta jadadda farin cikin bisa yadda al’ummar kasar nan ke baiwa gwamnatin Buhari goyon baya.
Tace ta shirya shiga cikin kwamitin yakin neman sake zabar mai gidan na ta ne sakamakon hangen da ta yi na abubuwan alhairi da wannan gwmanati ke samawa matasan kasar nan.
Hajiya Aisha Buhari tace zuwa yanzu Gwamnatin Muhammadu Buhari ta bujiro da ayyuka iri daban daban domin koyawa mata da matasa sana’u iri daban daban, tare raba masu tallafi, haka kuma akwai wani tsari wanda ke gudana karkashin ofishin mataimakin Shigaban kasa Yemi Osinbajo wadda ake rabawa matasa Naira dunu talatin talatin domin fara dogoro da kansu, tace tana da yakinin wannan shiri idan aka Sake zabar Muhammadu Buhari za’a ci gaba da aiwatar da wannan kyakkyawan shiri.
Shi ma Gwamna Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya tabbatarwa da Shugaban kasa Muhammadu Buhari aniyar Jihar Kano na bashi kuri’a miliyon biyar a zabe shekara ta 2019, yace jama’ar Kano mutane masu godiya kuma nan ne cibiyar Jam’iyyr APC saboda haka muna da yakinin idan Allah ya kaimu lokacin zabe mai zuwa jihar Kao ce zata fara kawo sakamakon zaben wanda muke da yakinin Shugaban kasa Muhammadu Buhari ne zai lashe zaben.
Ita ma mai dakin Gwamnan Kano Dakta Hjaiya Hafsat Umar Ganduje ta bayyana sake zabar Muhammadu Buhari da Gwamna Ganduje a matasayin farar dabara, tace yanzu haka Jihar Kance Jiha daya Tilo data samarwa da mata masu tarin yawa sana’u da kuma jari a fannonin sana’a iri daban-daban, don haka sai ta godewa mai dakin shugaban kasar bisa zabar jihar Kano a matsayin wurin da za a kaddamar da yakin neman zaben shugaban Kasa a shekara ta 2019.
Cikin wadanda su ka dafawa matar shugaban kasar akwai matan gwamnonin jihohin Kano, Katsina, Kebbi, Kaduna, Jigawa da kuma mai dakin gwamna jihar Imo Rochas Okorocha a lokacin kaddamar da yakin neman zaben na shiyyar AREWA maso Yamma da a ka gudanar a babban dakin taro na Sani Abacha.
Source: hausa.leadership.ng
Da ta ke gabatar da Jawabinta awuri taron Hajiya Aisha Buhari ta jadadda farin cikin bisa yadda al’ummar kasar nan ke baiwa gwamnatin Buhari goyon baya.
Tace ta shirya shiga cikin kwamitin yakin neman sake zabar mai gidan na ta ne sakamakon hangen da ta yi na abubuwan alhairi da wannan gwmanati ke samawa matasan kasar nan.
Hajiya Aisha Buhari tace zuwa yanzu Gwamnatin Muhammadu Buhari ta bujiro da ayyuka iri daban daban domin koyawa mata da matasa sana’u iri daban daban, tare raba masu tallafi, haka kuma akwai wani tsari wanda ke gudana karkashin ofishin mataimakin Shigaban kasa Yemi Osinbajo wadda ake rabawa matasa Naira dunu talatin talatin domin fara dogoro da kansu, tace tana da yakinin wannan shiri idan aka Sake zabar Muhammadu Buhari za’a ci gaba da aiwatar da wannan kyakkyawan shiri.
Shi ma Gwamna Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya tabbatarwa da Shugaban kasa Muhammadu Buhari aniyar Jihar Kano na bashi kuri’a miliyon biyar a zabe shekara ta 2019, yace jama’ar Kano mutane masu godiya kuma nan ne cibiyar Jam’iyyr APC saboda haka muna da yakinin idan Allah ya kaimu lokacin zabe mai zuwa jihar Kao ce zata fara kawo sakamakon zaben wanda muke da yakinin Shugaban kasa Muhammadu Buhari ne zai lashe zaben.
Ita ma mai dakin Gwamnan Kano Dakta Hjaiya Hafsat Umar Ganduje ta bayyana sake zabar Muhammadu Buhari da Gwamna Ganduje a matasayin farar dabara, tace yanzu haka Jihar Kance Jiha daya Tilo data samarwa da mata masu tarin yawa sana’u da kuma jari a fannonin sana’a iri daban-daban, don haka sai ta godewa mai dakin shugaban kasar bisa zabar jihar Kano a matsayin wurin da za a kaddamar da yakin neman zaben shugaban Kasa a shekara ta 2019.
Cikin wadanda su ka dafawa matar shugaban kasar akwai matan gwamnonin jihohin Kano, Katsina, Kebbi, Kaduna, Jigawa da kuma mai dakin gwamna jihar Imo Rochas Okorocha a lokacin kaddamar da yakin neman zaben na shiyyar AREWA maso Yamma da a ka gudanar a babban dakin taro na Sani Abacha.
Source: hausa.leadership.ng








EmoticonEmoticon