Rahotanni sun bayyana cewa kungiyar kwallon kafa ta Barcelona ta cimma yarjejeniya da dan wasan kasar Faransa, Adrien Rabiot domin yakoma kungiyar a karshen kakar wasannan da ake bugawa.
Dan wasan dan kasar Faransa wanda baije gasar cin kofin duniya ba yanada damar tattaunawa da kungiyoyin da suke son daukarsa bayan da ya rage saura watanni shida kwantaraginsa ya kare da kungiyar ta PSG.
Kungiyoyin firimiya da suka hada da Liverpool da Tottenham da kuma kungiyar Arsenal dai sune suke zawarcin dan wasan sai dai daman tuni aka bayyana cewa yafison komawa Barcelona da buga wasa.
A satin daya gabata ne dai rahotanni suka bayyana cewa dan wasan ya kammala cimma yarjejeniya da dan wasan amma daga baya kungiyar ta karyata labarin inda ta bayyana cewa babu wata Magana tsakaninta da dan wasan.
Kawo yanzu dai tuni aka bayyana cewa Barcelona ta kammala Magana da dan wasan kuma zai koma bugawa kungiyar wasa idan an kammala kakar wasan da ake bugawa inda kuma zai karbi albashi mai yawa wanda ba’a bayyana ba.
Kungiyar PSG dai tayi kokarin sake sabuwar yarjejeniya da dan wasan sai dai rashin tabbacin buga wasanni akai-akai yasa dan wasan ya nuna bazai zauna ba kuma yana bukatar sabuwar kungiya.
Source: hausa.leadership.ng
Dan wasan dan kasar Faransa wanda baije gasar cin kofin duniya ba yanada damar tattaunawa da kungiyoyin da suke son daukarsa bayan da ya rage saura watanni shida kwantaraginsa ya kare da kungiyar ta PSG.
Kungiyoyin firimiya da suka hada da Liverpool da Tottenham da kuma kungiyar Arsenal dai sune suke zawarcin dan wasan sai dai daman tuni aka bayyana cewa yafison komawa Barcelona da buga wasa.
A satin daya gabata ne dai rahotanni suka bayyana cewa dan wasan ya kammala cimma yarjejeniya da dan wasan amma daga baya kungiyar ta karyata labarin inda ta bayyana cewa babu wata Magana tsakaninta da dan wasan.
Kawo yanzu dai tuni aka bayyana cewa Barcelona ta kammala Magana da dan wasan kuma zai koma bugawa kungiyar wasa idan an kammala kakar wasan da ake bugawa inda kuma zai karbi albashi mai yawa wanda ba’a bayyana ba.
Kungiyar PSG dai tayi kokarin sake sabuwar yarjejeniya da dan wasan sai dai rashin tabbacin buga wasanni akai-akai yasa dan wasan ya nuna bazai zauna ba kuma yana bukatar sabuwar kungiya.
Source: hausa.leadership.ng


EmoticonEmoticon