Gwamnatin tarayyar Nijeriya ta ce, zaman tattaunawa a tsakaninta da kungiyar malaman jami’o’i ta kasa (ASUU) zai ci gaba da gudanuwa a gobe Litinin domin ci gaba da neman shawo kan yajin aikin da kungiyar ke ci gaba da yi domin ganin an shawo kan matsalar.
Ministan ayyuka, Sanata Chris Ngege shine ya shaida hakan a cikin sanarwarsa da ya rabar wa ‘yan jarida a jiya Asabar, wanda Daraktan yada labaran ma’aikatar Mista Samuel Olowookere, ya rattaba wa hanu.
Kamar yadda sanarwar ke cewa, zaman gawar za a yi ta ne domin shawo kan yajin aikin da kuma tattauna yadda za a yi kungiyar ta koma bakin aikinta.
Sanarwar take cewa; “Ministan aiyuka Sen. Chris Ngige ya tsara ganawa da shugabanin kungiyar ASUU domin tattauna yadda za a samu bakin zaren shawo kan yajin aikin da suke yi.
Za a yi ganawar ne a ranar 7 ga watan Janairun 2019 a dakin taro na ma’aikatar aiyuka da misalin karfe 20:30 na dare daidai,” Inji sanarwar.
Kamfanin dallancin labarai ta kasa NAN ta habarto cewar ASUU dai ta shiga yajin aikin sai baba ta gani ne tun a ranar 5 ga watan Nuwamban 2018 biyo bayan gaza cika musu alkawuran da suka yi da gwamnati tun a shekarar 2009.
Source: hausa.leadership.ng
Ministan ayyuka, Sanata Chris Ngege shine ya shaida hakan a cikin sanarwarsa da ya rabar wa ‘yan jarida a jiya Asabar, wanda Daraktan yada labaran ma’aikatar Mista Samuel Olowookere, ya rattaba wa hanu.
Kamar yadda sanarwar ke cewa, zaman gawar za a yi ta ne domin shawo kan yajin aikin da kuma tattauna yadda za a yi kungiyar ta koma bakin aikinta.
Sanarwar take cewa; “Ministan aiyuka Sen. Chris Ngige ya tsara ganawa da shugabanin kungiyar ASUU domin tattauna yadda za a samu bakin zaren shawo kan yajin aikin da suke yi.
Za a yi ganawar ne a ranar 7 ga watan Janairun 2019 a dakin taro na ma’aikatar aiyuka da misalin karfe 20:30 na dare daidai,” Inji sanarwar.
Kamfanin dallancin labarai ta kasa NAN ta habarto cewar ASUU dai ta shiga yajin aikin sai baba ta gani ne tun a ranar 5 ga watan Nuwamban 2018 biyo bayan gaza cika musu alkawuran da suka yi da gwamnati tun a shekarar 2009.
Source: hausa.leadership.ng


EmoticonEmoticon