Wednesday, 16 January 2019

Adamu Mohammed Ne Sabon Sufeton ‘Yan Sanda

Tags

Shugaba Muhammadu Buhari ya nada Mohammed Adamu matsayin sabon Sufeton ‘Yan Sanda na kasa.

Bayani na nuna cewa, in har ba a samu wani canji na gaggauwa ba fadar shugaban kasar za ta bayar da cikkaken sanarwa nadin yau Talata, wanda shi ne zai maye gurbin Ibrahim Idris wanda yake kammala aikinsa jiya Litinin.

Bayani ya nuna cewa, Shugaba Buhari ya yanke shawarar nada sabon sufeton ne bayan da aka ci gaba da samun matsin lamba daga jam’iyyun adawa in da suke korafin cewa, na neman a tsawaita aikin shugaban ‘yan sanda ne saboda a samu daman murde harkar zaben da za gudanar a cikin wannna shekarar.

Bayanin ya kuma ci gaba cewa, tuni shugaban kasar ya yanke shawarar wanda za nada a matsayin sufeto janar na ‘yan sandan ya kuma yanke shawarar rashin tsawaita zamanin aikin Idri Ibrahim da aikin nasa ke karewa.

Mista Mohammed, da aka fi sani da Mohammed Lafia, kafin wannan nadin shi ne mataimakin sufeto janar mai kula da yankin na 5 na rundunar ‘yan sanda na kasa.

Mista Mohammed, dan asalin garin Lafia, ya jijhar Nasarawa, an kuma haife shi ne a ranar 9 ga watan Nobamba 1961.

Ya shiga aikin dan sana ne a shekakar 1986. Ya kuma yi aikid a rundunar samar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya, ya kuma rike mukanin Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Inugu.
Source: hausa.leadership.ng


EmoticonEmoticon