Jami’an tsaro na farin kaya ta (DSS) ta bayyana cewar ta kwantar da Sanata Dino Melaye a cikin asibitinta da ke Abuja domin ci gaba da samar masa da lafiya da kuma taimaka wa ‘yan sanda kan yanayin nasa.
A cikin wata kwafin sanarwar manema labaru da Kakakin DSS, Peter Afunnaya ya fitar, yana mai bayyana cewar ‘yan sandan sun kawo Dino Melaye cikin asibitin DSS ne biyo bayan samun izinin tsareshi na kwanaki 14 wanda ya fara aiki tun daga ranar 9 ga watan Janairun 2019.
A cewar shi, “Abun da ya sanya aka kawo shi asibitinmu, shine domin taimaka wa ‘yan sanda wajen baiwa shi Sanata Dino kulawar jinya da yake bukata,” Inji Sanarwar Ya kuma kara da cewa, “Sanatan yana samun kyakkyawar kulawa ta kwararrun likitoci a sakamakon hadin kai da ake samu daga gareshi,” Inji DSS Peter Afunnaya ya ce, sun fitar da wannan sanarwar ne a bisa dole, domin warware shubuhar wasu bayanai na karya da suka basu da ke zargin jami’an DSS da sace Sanata Melaye daga hanun ‘yan sanda a asibiti.
Ya kuma ce, DSS tana mai bayar da tabbaci wa jama’an kasa na ci gaba da gudunar da aikinta bisa kwarewa da sanin hakkin dan adam ba tare da tauye ma wani hakkinsa na rayuwa ko walwala ba.
Source: hausa.leadership.ng
A cikin wata kwafin sanarwar manema labaru da Kakakin DSS, Peter Afunnaya ya fitar, yana mai bayyana cewar ‘yan sandan sun kawo Dino Melaye cikin asibitin DSS ne biyo bayan samun izinin tsareshi na kwanaki 14 wanda ya fara aiki tun daga ranar 9 ga watan Janairun 2019.
A cewar shi, “Abun da ya sanya aka kawo shi asibitinmu, shine domin taimaka wa ‘yan sanda wajen baiwa shi Sanata Dino kulawar jinya da yake bukata,” Inji Sanarwar Ya kuma kara da cewa, “Sanatan yana samun kyakkyawar kulawa ta kwararrun likitoci a sakamakon hadin kai da ake samu daga gareshi,” Inji DSS Peter Afunnaya ya ce, sun fitar da wannan sanarwar ne a bisa dole, domin warware shubuhar wasu bayanai na karya da suka basu da ke zargin jami’an DSS da sace Sanata Melaye daga hanun ‘yan sanda a asibiti.
Ya kuma ce, DSS tana mai bayar da tabbaci wa jama’an kasa na ci gaba da gudunar da aikinta bisa kwarewa da sanin hakkin dan adam ba tare da tauye ma wani hakkinsa na rayuwa ko walwala ba.
Source: hausa.leadership.ng



EmoticonEmoticon