Sanata Dino Melaye mai wakiltan Kogi ta yamma da ke cigaba da buya ya fadi dalilin da yasa ba zai mika kansa ga hukumar 'yan sandan Najeriya ba.
Mr Melaye ya yi ikirarin cewa Sufeta Janar na 'yan sanda, Ibrahim Idris yana son yasa ayi masa allurar guba da zata kashe shi muddin ya mika kansa ga 'yan sandan hakan yasa ya cigaba da buya.
Sanatan ya kwatanta halin da ya shiga a yanzu da gwagwarmayar da Annabi Elijah ya yi a littafin Bible mai tsarki a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter a daren ranar Talata.
Premium Times ta ruwaito a baya yadda 'yan sandan suka mamaye gidan Dino Melaye da ke Abuja a ranar Juma'a inda suka ce ana tuhumarsa da hannu cikin fashi da makami da shirya kisan kai.
Wannan dai shine karo na hudu da jami'an yan sanda su kayi yunkurin kama Dino Melaye a cikin shekarar 2018 da ta gabata.
A sakon da mai magana da yawun 'yan sanda Jimoh Moshood ya fitar, ya ce Dino Melaye tare da 'yan dabarsa sun harbi wani jami'in dan sanda mai mukamamin Saja, Danjuma Saliu a watan Yulin 2018.
A maimakon ya karyata zargin da 'yan sanda ke masa, Dino Melaye kawai ya ce hikima ce ta sa ya cigaba da kasancewa a inda ya ke buya amma ba tsoro ba.
Melaye ya ce Annabi Elijah yana daya daga cikin Annabawa masu karfi a cikin Bible amma ya tafi Dutsen Carmel ya buya a lokacin da Sarki Ahab ke nemansa domin ya kashe shi saboda ya fadi gaskiya.
Source: hausa.legit.ng
Mr Melaye ya yi ikirarin cewa Sufeta Janar na 'yan sanda, Ibrahim Idris yana son yasa ayi masa allurar guba da zata kashe shi muddin ya mika kansa ga 'yan sandan hakan yasa ya cigaba da buya.
Sanatan ya kwatanta halin da ya shiga a yanzu da gwagwarmayar da Annabi Elijah ya yi a littafin Bible mai tsarki a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter a daren ranar Talata.
Premium Times ta ruwaito a baya yadda 'yan sandan suka mamaye gidan Dino Melaye da ke Abuja a ranar Juma'a inda suka ce ana tuhumarsa da hannu cikin fashi da makami da shirya kisan kai.
Wannan dai shine karo na hudu da jami'an yan sanda su kayi yunkurin kama Dino Melaye a cikin shekarar 2018 da ta gabata.
A sakon da mai magana da yawun 'yan sanda Jimoh Moshood ya fitar, ya ce Dino Melaye tare da 'yan dabarsa sun harbi wani jami'in dan sanda mai mukamamin Saja, Danjuma Saliu a watan Yulin 2018.
A maimakon ya karyata zargin da 'yan sanda ke masa, Dino Melaye kawai ya ce hikima ce ta sa ya cigaba da kasancewa a inda ya ke buya amma ba tsoro ba.
Melaye ya ce Annabi Elijah yana daya daga cikin Annabawa masu karfi a cikin Bible amma ya tafi Dutsen Carmel ya buya a lokacin da Sarki Ahab ke nemansa domin ya kashe shi saboda ya fadi gaskiya.
Source: hausa.legit.ng


EmoticonEmoticon