Hukumar bayar da lambar sheda ta kasa ta NIMC ta sanar da cewar, yin amfani da lambar sheda ta kasa ta NIN a tsakanin hukumimin gwamnati za ta fara aiki daga ranar daya ga watan Janairun shekarar 2018.
Darakta Janar na hukumar ta NIMC, Aliyu Aziz ne ya sanar da hakan, inda ya ce, hakan ya nuna cewar, ma’aikatun gwamnati, hukumimi da kuma sassa sun dauki bayanan sun kuma gabatar da lambar ta sheda saiko wanne dan kasa ya bukaci lambar kafin a gudanar masa da duk wani aiki da yake bukata.
Aliyu Aziz ya kuma baiwa yan Nijeriya tabbacin cewar, babu wani dan kasa da za’a haramta masa samu wani gudanar da aikin gwamnatin don bai mallaki lambar shedar ba.
Ya ci gaba da cewa, karbar lambar shedar ko tattara bayanan irin wadannan hukumomin gwamnati ko ajent dinsu da kuma fannin masana’antu masu zaman kansu da aka sanya su a cikin tsarin na hukumar, zai taimaka wajen tattara bayanan su.
Acewar sa, ma’aiakatun dakuma hukumomin, sun hadada, fannonin ilimi, Sufurin sama, ofishin shugabar ma’aiakata ta na kasa, ofishin Akuwa na tarayya, hukumar kididdigar alumma ta kasa, hukumar zabe, hukumar yin rijistar sana’oi ta kasa, hukumar tara haraji ta kasa da kuma hukumar sadarwa ta kasa.
Sauran ya ce, sun hadada, shirin lafiya na kasa, hukumar EFCC, hukumar shirya jarrabawa ta kasa JAMB, rundunar yansanda ta kasa da kuma hukumar musayar kudi ta kasa SEC.
Aliyu Aziz ya kara da cewa, hukumomin da aka zayyana a sama, dole ne su bukaci su kuma tantance lambar shedar ta NIN wadda tuni aka amice da ita a tsarin hada-hadar bankun na kasar nan, hukumar kula shege da fece ta kasa, hukumar kiyaye hadurra ta kasa da kuma hukumar fansho ta kasa.
Ya sanar da cewar Shugaban kasa Muhammadu Buhari da kuma majalisar zantarwa ta kasa tuni suka amince da sabon tsarin na NDIESR don sanya yan Nijeriya da kuma mazauna don a sanya su a cikin bayanan na shedar.
Aliyu Aziz ya kara da cewa, “an dora mana nauyin yiwa daukacin yan Nijeriya rijista da kuma wadanda suka zaune a cikin kasar a bisa izinin hukuma ko kuma a kalla sama da kashi 95 bisa dari na alummar kasar nan a cikin shekaru uku masu zuwa.
Ya bayyana cewar, ba wai lallai bane sai hukumar ta kakkafa cibiyoyi da ofishoshi a daukacin fadin kasar nan ba, musamman idan aka yi la’akari da halin tattalin aezikin kasa da ake fuskanta a yanzu.
A bisa tausayi na gwamnatin tarayya, ta amince da sabon tsarin na NDIESR wanda zai tabbar da kuma dorawa dukkan ma’aikatun gwamnati da hukumomin da aka zayyana a sama da kuma masana’antu masu zaman kansu na hukumar ta yi masu lasisi da hukumar don tattara bayanan yan kasa ta hanyar basu lambar shedar ta kasa.
Source: hausa.leadership.ng
Darakta Janar na hukumar ta NIMC, Aliyu Aziz ne ya sanar da hakan, inda ya ce, hakan ya nuna cewar, ma’aikatun gwamnati, hukumimi da kuma sassa sun dauki bayanan sun kuma gabatar da lambar ta sheda saiko wanne dan kasa ya bukaci lambar kafin a gudanar masa da duk wani aiki da yake bukata.
Aliyu Aziz ya kuma baiwa yan Nijeriya tabbacin cewar, babu wani dan kasa da za’a haramta masa samu wani gudanar da aikin gwamnatin don bai mallaki lambar shedar ba.
Ya ci gaba da cewa, karbar lambar shedar ko tattara bayanan irin wadannan hukumomin gwamnati ko ajent dinsu da kuma fannin masana’antu masu zaman kansu da aka sanya su a cikin tsarin na hukumar, zai taimaka wajen tattara bayanan su.
Acewar sa, ma’aiakatun dakuma hukumomin, sun hadada, fannonin ilimi, Sufurin sama, ofishin shugabar ma’aiakata ta na kasa, ofishin Akuwa na tarayya, hukumar kididdigar alumma ta kasa, hukumar zabe, hukumar yin rijistar sana’oi ta kasa, hukumar tara haraji ta kasa da kuma hukumar sadarwa ta kasa.
Sauran ya ce, sun hadada, shirin lafiya na kasa, hukumar EFCC, hukumar shirya jarrabawa ta kasa JAMB, rundunar yansanda ta kasa da kuma hukumar musayar kudi ta kasa SEC.
Aliyu Aziz ya kara da cewa, hukumomin da aka zayyana a sama, dole ne su bukaci su kuma tantance lambar shedar ta NIN wadda tuni aka amice da ita a tsarin hada-hadar bankun na kasar nan, hukumar kula shege da fece ta kasa, hukumar kiyaye hadurra ta kasa da kuma hukumar fansho ta kasa.
Ya sanar da cewar Shugaban kasa Muhammadu Buhari da kuma majalisar zantarwa ta kasa tuni suka amince da sabon tsarin na NDIESR don sanya yan Nijeriya da kuma mazauna don a sanya su a cikin bayanan na shedar.
Aliyu Aziz ya kara da cewa, “an dora mana nauyin yiwa daukacin yan Nijeriya rijista da kuma wadanda suka zaune a cikin kasar a bisa izinin hukuma ko kuma a kalla sama da kashi 95 bisa dari na alummar kasar nan a cikin shekaru uku masu zuwa.
Ya bayyana cewar, ba wai lallai bane sai hukumar ta kakkafa cibiyoyi da ofishoshi a daukacin fadin kasar nan ba, musamman idan aka yi la’akari da halin tattalin aezikin kasa da ake fuskanta a yanzu.
A bisa tausayi na gwamnatin tarayya, ta amince da sabon tsarin na NDIESR wanda zai tabbar da kuma dorawa dukkan ma’aikatun gwamnati da hukumomin da aka zayyana a sama da kuma masana’antu masu zaman kansu na hukumar ta yi masu lasisi da hukumar don tattara bayanan yan kasa ta hanyar basu lambar shedar ta kasa.
Source: hausa.leadership.ng



EmoticonEmoticon